Skip to main content

INA MA TSAYAR HAUSAWAN JOS A SIYASA?

Al’ummar Hausawa musamman wanda suke zaune a cikin birnin garin Jos ta arewa, sun kasance masu bada gudumawa wajen cigaban jahar Filato a fani daban daban kama daga kasuwanci, zamantakewa, hada har da siyasa, amma babban abun tamabaya anan shine ko shin su al’ummar ina suka dosa, ko muce ina tasu tsayar su a siyasar dubu biyu da ashirn da uku (2023). Amma bari muyi duba da irin gudumawar da suka bayar wajen kafuwar gwamnatin Lalong IRIN GUDUMAWAR DA SUKA BAYAR WAJEN KAFA GWAMNATIN LALONG A sheharar dubu biyu da goma sha biyar al'ummar Hausawan garin Jos suka bada gudumawa sosai wajen kafa gwamnati maici a karkashin Rt. Honorable Simon Lalong inda suka bashi kuri’a mafi tsoka wanda ku shi, Gwamnan naji shi ya sha fadin cewa badan kuri’ar suba da laile ba zai kawo gaci ba. inda kuma yayi alkwarin saka masu da romon demokaradiyya. Ko shin ya saka masu? Bari muyi duba da irin alkawarin da ya dauka masu kafin hauwar sa mulki.

1. GYARA BABBAR KASUWAR TERMINUS A yayin da yake neman kujerar gwamna a 2015 Simon Lalong yayi alkwarin cewa zai gyara ita wanna kasuwa, domin kasuwanci ya bunkasa tare da rage rashin aikin yi, amma tun bayan da ya hau kan karagar mulki ba wani abu zo a gani da za'a ace an sake ji mai inganci game da gyara kasuwar, sai dai a wani lokacin da ake daf da zaben 2019, Gwamna Lalong ya waiwaye ita wannan kasuwa inda ya fadawa al’ummar Jos ta arewa cewa yanzu an gama komai da wanda zasu gyara kasuwar har an ware Naira Biyon Daya wajen rusa kasuwar. Amma tunda aka rusa wani yanki na kasuwar har yanzu ba ko motar kasa daya da aka kawo, sai dai ma zargin gwamnatin Lalong da salwantar da karafen da aka cire a yayin rusa wani ban gare na kasuwar. Amma kuma acikin shekarar 2022 aka kara jin cewa wai Gwamnatin jahar filato tare da hadin gwiwar bankin muslunci wato Jaiz zata gyara kasuwar wanda har yazu ba a sake ji ko ina maganar ta kwana ba. Zamu iya cewa dai kawai gwamantin Lalong tayi kokari wajen yaudarar al’ummar Jos musamman hausawa wajen neman kuri’ar suba tare da ta cika masu wannan alkawarin ba. A hira da mukayi da wasu mazauna kasuwar sun nuna cewa tabbas da za’a gyara wannan kasuwar da ta kawo cigaba ma jahar Filato da ma kasa baki daya, amma sun danganta kin gyarawar da baya rasa nasaba da kabilanci duba da yarda cewa su hausawan sune mafi amfana da wannan kasuwa. 


 2. BUNKASA CIKIN BIRNIN JOS Wani daga cikin alkwarin da gwamnatin APC mai mulki tayi wa al’ummar Hausawan Jos shine bunkasa cikin garin da hanyoyi tare da kuma kara fadin garin, amma bisa dukkan alamu dai wannan alkawarin shima yana kokarin zama tarihi kamar yarda sauran yan siyasa suke ma jama’a. Domin zamu iya cewa banda titin Anguwan rogo wanda shima kasa da kilomita shida da ya dauki gwamnatin sama da shekara biyu kafin ta kammala ba wani abun azo a gani da za’ace ta aiwatar ma al’ummar Hausawan Jos. A lokacin da damuna take kara kusantuwa acikin garin Jos yana kasancewa mafi kazanta a duk sanda akayi ruwan sama, domin bayan ruwa ya sauka manyan titunan garin kan cika da shara da sauran datti dake barazana ga lafiyar yanki. Bayan nan wanda ya bar garin Jos shekara ashirn idan ya dawo zai iya kama hanyar zuwa gida domin kuwa yarda yabar garin hakan zai dawo ya same sa ba tare da wani alamun samun chanji ba, akan hanyiyoyi.

Comments

  1. Allah ya kyauta. Amma dai kam ya kamata alumma su lura wajen zaben shugabani

    ReplyDelete
  2. Maganar Mai magana ta farko Mai rubutu Yakoma baya lokachin da akeneman afara gyara Mai mutanen gari suke Chewa,har zanga zanga sukayi SUNA fadin basu yarda ba.

    ReplyDelete
  3. Ubangiji Allah ya kyauta, kuma yasa mu matasa mu gane yancinmu a koda wannane lokaci kuri’armu yancinmu

    ReplyDelete
  4. Wllhi especially government school, primary school , & secondary school, wllhi kullum yau I jiya, education system nothing nothing

    ReplyDelete

Post a Comment

Popular posts from this blog

All Is Set For APC Presidential Primary.

All is now set for the All Progressives Congress (APC) Presidential primary in Abuja holding from Monday, June 6 to June 7 at the Eagle’s Square with six aspirants in the lead, Jasawa Times learned. The presidentail aspirant include the Vice-President Yemi Osibanjo; former Minister of Science and Technology, Ogbonnaya Onu, Ebonyi Gov. Dave Umahi; former Lagos Gov. Bola Ahmed Tinubu, former Minister of Transportation, Rotimi Amaechi and ex-Minister of State for Education, Chief Chukwuemeka Nwajiuba. The Eagles Square is expected to host about 2,240 delegates from the 36 states and the Federal Capital Territory. Expectedly, the influx of people into the FCT has increased, a development that has attracted more police presence at the Eagles Square and some hotels hosting the delegates and chieftains of the APC. Ahead of the event, the party’s National Chairman, Sen.Abdullahi Adamu on Sunday visited the Eagles Square where he expressed satisfaction with the facilities put in place by...

2023 ELECTION: BVAS mock accreditation Feb 4… INEC

The Independent National Electoral Commission (INEC) has said that it would conduct a mock accreditation of registered voters in 436 polling units (PUs) nationwide, on February 4 using its Bimodal Voter Accreditation System (BVAS) machines. The INEC Chairman, Prof. Mahmood Yakubu, said this during a meeting with Resident Electoral Commissioners (RECs) on Friday in Abuja. He said that 436 Bimodal Voter Accreditation System (BVAS) machines would be deployed for the exercise. “As you are already aware, the commission has taken delivery of the BVAS machines for the election. We have also dutifully tested each machine in our offices nationwide to ensure its functionality. “The next step is to conduct field tests across the country involving actual voters. For this reason, and in readiness for nationwide deployment, the commission is conducting a mock accreditation of voters similar to what was done ahead of the recent Ekiti and Osun states governorship elections. “The mock accreditation wil...

Concern PDP Muslim Youth Council paid a courtesy visit to Plateau State Governor-elect.

A coalition Muslim PDP Youth in Plateau state called Concern PDP Muslim Youth Council paid a congratulatory visit to Plateau Satet Governor-elect Barrister Caleb Mutgwang. Leading the delegation Hon. Kabiru Garkuwa, while delivering the Goodwill message  stated that the Council embarked on the visit to thank the Governor and show their unwavering faith and support for the victory at the recently concluded election. In his speech, Garkuwa, “Praised God for the glorious victory achieved by our dear Party PDP in general elections”  He also Added that, “with the like of his Excellency's at the helm of affairs in governance, Plateau State will be in safe hands”. He as well commended the commitments and the sacrifices of Hon. Yary Kumci, appreciated his kind support and benevolence always accorded to the group.  Garkuwa while presenting a letter to Governor elect.  Garkuwa also appreciate other officials among are   Hajiya Jamila Gwandu, Alh. Aminu Abdullahi (Jos...