Skip to main content

INA MA TSAYAR HAUSAWAN JOS A SIYASA?

Al’ummar Hausawa musamman wanda suke zaune a cikin birnin garin Jos ta arewa, sun kasance masu bada gudumawa wajen cigaban jahar Filato a fani daban daban kama daga kasuwanci, zamantakewa, hada har da siyasa, amma babban abun tamabaya anan shine ko shin su al’ummar ina suka dosa, ko muce ina tasu tsayar su a siyasar dubu biyu da ashirn da uku (2023). Amma bari muyi duba da irin gudumawar da suka bayar wajen kafuwar gwamnatin Lalong IRIN GUDUMAWAR DA SUKA BAYAR WAJEN KAFA GWAMNATIN LALONG A sheharar dubu biyu da goma sha biyar al'ummar Hausawan garin Jos suka bada gudumawa sosai wajen kafa gwamnati maici a karkashin Rt. Honorable Simon Lalong inda suka bashi kuri’a mafi tsoka wanda ku shi, Gwamnan naji shi ya sha fadin cewa badan kuri’ar suba da laile ba zai kawo gaci ba. inda kuma yayi alkwarin saka masu da romon demokaradiyya. Ko shin ya saka masu? Bari muyi duba da irin alkawarin da ya dauka masu kafin hauwar sa mulki.

1. GYARA BABBAR KASUWAR TERMINUS A yayin da yake neman kujerar gwamna a 2015 Simon Lalong yayi alkwarin cewa zai gyara ita wanna kasuwa, domin kasuwanci ya bunkasa tare da rage rashin aikin yi, amma tun bayan da ya hau kan karagar mulki ba wani abu zo a gani da za'a ace an sake ji mai inganci game da gyara kasuwar, sai dai a wani lokacin da ake daf da zaben 2019, Gwamna Lalong ya waiwaye ita wannan kasuwa inda ya fadawa al’ummar Jos ta arewa cewa yanzu an gama komai da wanda zasu gyara kasuwar har an ware Naira Biyon Daya wajen rusa kasuwar. Amma tunda aka rusa wani yanki na kasuwar har yanzu ba ko motar kasa daya da aka kawo, sai dai ma zargin gwamnatin Lalong da salwantar da karafen da aka cire a yayin rusa wani ban gare na kasuwar. Amma kuma acikin shekarar 2022 aka kara jin cewa wai Gwamnatin jahar filato tare da hadin gwiwar bankin muslunci wato Jaiz zata gyara kasuwar wanda har yazu ba a sake ji ko ina maganar ta kwana ba. Zamu iya cewa dai kawai gwamantin Lalong tayi kokari wajen yaudarar al’ummar Jos musamman hausawa wajen neman kuri’ar suba tare da ta cika masu wannan alkawarin ba. A hira da mukayi da wasu mazauna kasuwar sun nuna cewa tabbas da za’a gyara wannan kasuwar da ta kawo cigaba ma jahar Filato da ma kasa baki daya, amma sun danganta kin gyarawar da baya rasa nasaba da kabilanci duba da yarda cewa su hausawan sune mafi amfana da wannan kasuwa. 


 2. BUNKASA CIKIN BIRNIN JOS Wani daga cikin alkwarin da gwamnatin APC mai mulki tayi wa al’ummar Hausawan Jos shine bunkasa cikin garin da hanyoyi tare da kuma kara fadin garin, amma bisa dukkan alamu dai wannan alkawarin shima yana kokarin zama tarihi kamar yarda sauran yan siyasa suke ma jama’a. Domin zamu iya cewa banda titin Anguwan rogo wanda shima kasa da kilomita shida da ya dauki gwamnatin sama da shekara biyu kafin ta kammala ba wani abun azo a gani da za’ace ta aiwatar ma al’ummar Hausawan Jos. A lokacin da damuna take kara kusantuwa acikin garin Jos yana kasancewa mafi kazanta a duk sanda akayi ruwan sama, domin bayan ruwa ya sauka manyan titunan garin kan cika da shara da sauran datti dake barazana ga lafiyar yanki. Bayan nan wanda ya bar garin Jos shekara ashirn idan ya dawo zai iya kama hanyar zuwa gida domin kuwa yarda yabar garin hakan zai dawo ya same sa ba tare da wani alamun samun chanji ba, akan hanyiyoyi.

Comments

  1. Allah ya kyauta. Amma dai kam ya kamata alumma su lura wajen zaben shugabani

    ReplyDelete
  2. Maganar Mai magana ta farko Mai rubutu Yakoma baya lokachin da akeneman afara gyara Mai mutanen gari suke Chewa,har zanga zanga sukayi SUNA fadin basu yarda ba.

    ReplyDelete
  3. Ubangiji Allah ya kyauta, kuma yasa mu matasa mu gane yancinmu a koda wannane lokaci kuri’armu yancinmu

    ReplyDelete
  4. Wllhi especially government school, primary school , & secondary school, wllhi kullum yau I jiya, education system nothing nothing

    ReplyDelete

Post a Comment

Popular posts from this blog

NGF Promises Improved Minimum Wage Amid Ongoing Negotiations

The Nigeria Governors' Forum (NGF) has assured Nigerians and organized labor that negotiations are underway to establish a better minimum wage. This comes after the governors previously rejected the Federal Government's proposal of N62,000, citing that some states would need to borrow to pay salaries. Despite this, organized labor continues to push for a wage of N250,000. Nigeria Governor's Forum  Following the Federal Executive Council's postponement of the minimum wage discussion, the governors held an emergency meeting, which extended into the early hours of Thursday. According to a communiqué signed by NGF acting Director, Media, Ahmed Salihu, the forum discussed various national issues, including the new national minimum wage. The governors agreed to continue engaging with key stakeholders to reach a mutually acceptable solution, assuring that better wages will result from the ongoing negotiations. They also discussed the World Bank-Nigeria for Women Project Scale-

JUST NOW: Woman Caught with Stolen AK-47

Security forces apprehended a middle-aged woman, Aisha Abubakar, from Katsina State, while she was on a bus traveling to Abuja from Katsina. The woman was found in possession of a stolen AK-47 rifle, prompting her arrest. Suspected Aisha Abubakar  During interrogation, Aisha revealed that she was driven by extreme hunger and desperation to accept the task from unknown individuals. She claimed that she was instructed to transport the weapon to a designated location near Yantumaki, where the owners would retrieve it. Aisha maintained that this was her first involvement in such a dangerous and illegal activity, and that her dire circumstances left her with little choice but to accept the job. Her statement highlights the devastating impact of poverty and hunger on individuals, leading them to engage in illicit activities out of desperation.

Tragedy at the National Assembly: Customs Officer Passes Away

Tragedy struck at the National Assembly on Tuesday when a senior officer of the Nigeria Customs Service passed away during a meeting with a House Committee. According to a statement released by House Spokesman Akin Rotimi, the officer suddenly fell ill at approximately 1 pm and despite prompt medical attention from first responders and the National Assembly Clinic's medical team, sadly succumbed to his condition. Nass Out of respect for the family's privacy, the officer's identity has not been disclosed at this time. The House of Representatives extends its heartfelt condolences to the family, friends, and colleagues of the deceased and stands ready to support investigations into the circumstances surrounding the incident.