Skip to main content

GWAMNA ADELEKE NA JIHAR OSUN ZAI ƊAUKAKA ƘARA KAN HUKUNCIN KOTU

Gwamnan jihar Osun, Sanata Ademola Adeleke ya ce zai ɗaukaka ƙara game da hukuncin da kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓe ta yanke, inda ta soke zaɓen da aka yi masa a matsayin gwamna.

Acikin martanin da ya yi ta hannun mai magana da yawunsa, Mallam Olawale Rasheed, Adeleke na jam’iyyar PDP

ya bayyana hukuncin kotun a matsayin kuskure.

Ya ce lamarin rashin adalci ne, wanda ya ci karo da muradin mafi yawan al’ummar jiohar.

A ranar jumu’ar nan ne kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓe ta soke zaɓen da aka yi wa Ademola Adeleke na jam’iyyar PDP a matsayin gwamnan jihar Osun.

Kotun ta kuma ce tsohon gwamnan jihar, Adegboyega Oyetola na jam’iyyar APC ne ya lashe zaɓen idan aka yi la’akari da yawan ƙuri’un da aka kaɗa bayan kawar da ƙuri’un da aka yi aringizo.

A lokacin da yake yanke hukuncin, Mai shari’a Tetsea Kume, ya ce Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa,  INEC ba ta bi tanade-tanaden dokar zaɓe da na Ƙundin tsarin mulki yadda ya kamata ba.

A cewar kotun, idan aka cire ƙuri’un da ake zargin an yi aringizo, Adegboyega Oyetola na APC ya samu yawan ƙuri’u 314,921 yayin da Ademola Adeleke na PDP ya samu ƙuri’u 290,266.

Gwamna Adeleke ya buƙaci magoya bayansa su kwantar da hankalinsu, kuma a cewar sa, har yanzu shi ne halastaccen gwamnan jihar.

Comments

Popular posts from this blog

Bridging Digital Divides: Empowering People with Special Needs and Uniting Communities Through Technology

By Abdullahi Abdulhafiz Aliyu In today’s fast-changing digital landscape, access to technology is no longer a luxury—it is a necessity. Yet, for millions of Nigerians, especially people with special needs, the digital world remains out of reach due to systemic barriers and a lack of inclusive learning opportunities. My work as a journalist and digital advocate has focused on breaking these barriers, ensuring that technology serves as a tool for empowerment rather than exclusion. Through my engagement with individuals with disabilities and as the host of Duniyar Fasaha (Fasaha World) on Unity FM, I have worked to bridge the digital divide by providing foundational digital education to marginalized groups. By introducing people with special needs to basic computer skills such as Microsoft Word, Excel, PowerPoint, and internet navigation, I have witnessed firsthand how technology can unlock new opportunities and transform lives. Digital Skills for Special Needs: A Path to Inclusion Inclu...

Yanzu yanzu: 'yan majalisar dattijai sun tafi hutu domin gudanar da yaƙin neman zaɓe

Majalisar dattijan Nigeria, sun tafi hutu a yau Laraba, domin samun cigaba da gudanar da harkokin yaƙin neman zaɓe a jam'iyyun da suke ciki, don tunkarar babban zaɓen shekarar 2023, kamar yadda shugaban majalisar, Sanata Ahmad Lawan, ya bayyana yayin zaman majalisar na wannan rana. Lawan yace zace zasu tafi hutun ne domin tabbatar da abubuwa sun zama cikin tsari a ƙasar nan, kuma za su dawo a ranar 28 ga watan Fabrairu, kwanaki uku kenan bayan an gudanar da zaɓen shugaban ƙasa dana yan majalisun tarayya, kafin su sake tafiya wani hutun a ranar 1 ga watan Maris, domin gudanar da zaɓen gwamnoni da yan majalisun dokokin jiha, da za'ayi a ranar 11 ga watan Maris. Cikin jawabinsa, Lawan yayi kira ga hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC, da kuma jami'an tsaro, akan su tabbatar sunyi ayyukansu yadda ya dace, domin yin zaɓe cikin kwanciyar hankali da lumana, karbabben zaɓe kuma sahihi. Majalisar Nigeriya

All Is Set For APC Presidential Primary.

All is now set for the All Progressives Congress (APC) Presidential primary in Abuja holding from Monday, June 6 to June 7 at the Eagle’s Square with six aspirants in the lead, Jasawa Times learned. The presidentail aspirant include the Vice-President Yemi Osibanjo; former Minister of Science and Technology, Ogbonnaya Onu, Ebonyi Gov. Dave Umahi; former Lagos Gov. Bola Ahmed Tinubu, former Minister of Transportation, Rotimi Amaechi and ex-Minister of State for Education, Chief Chukwuemeka Nwajiuba. The Eagles Square is expected to host about 2,240 delegates from the 36 states and the Federal Capital Territory. Expectedly, the influx of people into the FCT has increased, a development that has attracted more police presence at the Eagles Square and some hotels hosting the delegates and chieftains of the APC. Ahead of the event, the party’s National Chairman, Sen.Abdullahi Adamu on Sunday visited the Eagles Square where he expressed satisfaction with the facilities put in place by...