Skip to main content

Yanzu-Yanzu: Masu kutse sun sace Lambobin NIN din 'yan Najeriya sama da Miliyan 3

 


Sama da mutane miliyan uku ne aka sace NIN dinsu, bayan da wani dan kutse da aka fi sani da Sam ya kutsa NIMC.

Dan kutsen ya yi alfahari da cewa ya samu damar shiga garken hukumar gwamnatin Najeriya kuma yana iya ci gaba da yin duk abin da ya ga dama tare da wasu muhimman bayanai da ke hannun sa.

Kutsen da aka yi wa hukumar NIMC ba wai kawai ya fallasa raunin tsaron yanar gizo na Najeriya ba ne, har ma ya nuna irin hadarin da mazauna kasar ke ciki a halin yanzu.

Harin na intanet da aki ya zo ne kasa da watanni biyu da Hukumar Sadarwa ta Najeriya a watan Nuwamban 2021 ta yi gargadin cewa wata kungiyar kutse ta Iran na shirin yin leken asiri ta intanet a fadin Afirka.

Sanarwar da hukumar ta fitar ta kuma bayyana cewa, masu satar bayanan na kai hare-hare a kan kamfanonin sadarwa, da masu samar da intanet, da ma'aikatun harkokin wajen Najeriya da wasu kasashen Afirka.

Har ila yau, lamarin ya zo ne watanni bayan da gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari, a lokacin da ta umarci ‘yan Najeriya da su yi rajistar lambar dan kasa, ta yi ikirarin cewa za ta dakatar da laifukan da ake aikatawa a kasar ciki har da wadanda ake tafkawa ta hanyar Intanet.

Da yake jawabi a yayin kaddamar da tsarin inganta harkokin ‘yan kasa a bangaren sadarwa na Najeriya da kuma sake fasalin manufofin kasa na yin rajistar katin SIM a watan Mayun 2021, Shugaba Buhari ya ce, “NIN zai rufe daya daga cikin raunin da ke tattare da tsarin tsaro. Za mu iya ganowa da sanin halayen ’yan Najeriya cikin sauƙi.

"Za mu gano mutane cikin sauki, gami da 'yan damfara."

Da yake tabbatar wa ‘yan Najeriya muhimmancin sabon tsarin, Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Digital, Isa Pantami, a watan Yunin 2021, ya yi ikirarin cewa al’amuran ta’addanci irinsu ‘yan fashi da garkuwa da mutane sun ragu matuka a cikin kasar sakamakon haka dagewar da gwamnati ta yi na mutane a Najeriya su yi rajistar NIN.

Comments

Popular posts from this blog

Bridging Digital Divides: Empowering People with Special Needs and Uniting Communities Through Technology

By Abdullahi Abdulhafiz Aliyu In today’s fast-changing digital landscape, access to technology is no longer a luxury—it is a necessity. Yet, for millions of Nigerians, especially people with special needs, the digital world remains out of reach due to systemic barriers and a lack of inclusive learning opportunities. My work as a journalist and digital advocate has focused on breaking these barriers, ensuring that technology serves as a tool for empowerment rather than exclusion. Through my engagement with individuals with disabilities and as the host of Duniyar Fasaha (Fasaha World) on Unity FM, I have worked to bridge the digital divide by providing foundational digital education to marginalized groups. By introducing people with special needs to basic computer skills such as Microsoft Word, Excel, PowerPoint, and internet navigation, I have witnessed firsthand how technology can unlock new opportunities and transform lives. Digital Skills for Special Needs: A Path to Inclusion Inclu...

Yanzu yanzu: 'yan majalisar dattijai sun tafi hutu domin gudanar da yaƙin neman zaɓe

Majalisar dattijan Nigeria, sun tafi hutu a yau Laraba, domin samun cigaba da gudanar da harkokin yaƙin neman zaɓe a jam'iyyun da suke ciki, don tunkarar babban zaɓen shekarar 2023, kamar yadda shugaban majalisar, Sanata Ahmad Lawan, ya bayyana yayin zaman majalisar na wannan rana. Lawan yace zace zasu tafi hutun ne domin tabbatar da abubuwa sun zama cikin tsari a ƙasar nan, kuma za su dawo a ranar 28 ga watan Fabrairu, kwanaki uku kenan bayan an gudanar da zaɓen shugaban ƙasa dana yan majalisun tarayya, kafin su sake tafiya wani hutun a ranar 1 ga watan Maris, domin gudanar da zaɓen gwamnoni da yan majalisun dokokin jiha, da za'ayi a ranar 11 ga watan Maris. Cikin jawabinsa, Lawan yayi kira ga hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC, da kuma jami'an tsaro, akan su tabbatar sunyi ayyukansu yadda ya dace, domin yin zaɓe cikin kwanciyar hankali da lumana, karbabben zaɓe kuma sahihi. Majalisar Nigeriya

All Is Set For APC Presidential Primary.

All is now set for the All Progressives Congress (APC) Presidential primary in Abuja holding from Monday, June 6 to June 7 at the Eagle’s Square with six aspirants in the lead, Jasawa Times learned. The presidentail aspirant include the Vice-President Yemi Osibanjo; former Minister of Science and Technology, Ogbonnaya Onu, Ebonyi Gov. Dave Umahi; former Lagos Gov. Bola Ahmed Tinubu, former Minister of Transportation, Rotimi Amaechi and ex-Minister of State for Education, Chief Chukwuemeka Nwajiuba. The Eagles Square is expected to host about 2,240 delegates from the 36 states and the Federal Capital Territory. Expectedly, the influx of people into the FCT has increased, a development that has attracted more police presence at the Eagles Square and some hotels hosting the delegates and chieftains of the APC. Ahead of the event, the party’s National Chairman, Sen.Abdullahi Adamu on Sunday visited the Eagles Square where he expressed satisfaction with the facilities put in place by...