Skip to main content

Yanzu-Yanzu: Masu kutse sun sace Lambobin NIN din 'yan Najeriya sama da Miliyan 3

 


Sama da mutane miliyan uku ne aka sace NIN dinsu, bayan da wani dan kutse da aka fi sani da Sam ya kutsa NIMC.

Dan kutsen ya yi alfahari da cewa ya samu damar shiga garken hukumar gwamnatin Najeriya kuma yana iya ci gaba da yin duk abin da ya ga dama tare da wasu muhimman bayanai da ke hannun sa.

Kutsen da aka yi wa hukumar NIMC ba wai kawai ya fallasa raunin tsaron yanar gizo na Najeriya ba ne, har ma ya nuna irin hadarin da mazauna kasar ke ciki a halin yanzu.

Harin na intanet da aki ya zo ne kasa da watanni biyu da Hukumar Sadarwa ta Najeriya a watan Nuwamban 2021 ta yi gargadin cewa wata kungiyar kutse ta Iran na shirin yin leken asiri ta intanet a fadin Afirka.

Sanarwar da hukumar ta fitar ta kuma bayyana cewa, masu satar bayanan na kai hare-hare a kan kamfanonin sadarwa, da masu samar da intanet, da ma'aikatun harkokin wajen Najeriya da wasu kasashen Afirka.

Har ila yau, lamarin ya zo ne watanni bayan da gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari, a lokacin da ta umarci ‘yan Najeriya da su yi rajistar lambar dan kasa, ta yi ikirarin cewa za ta dakatar da laifukan da ake aikatawa a kasar ciki har da wadanda ake tafkawa ta hanyar Intanet.

Da yake jawabi a yayin kaddamar da tsarin inganta harkokin ‘yan kasa a bangaren sadarwa na Najeriya da kuma sake fasalin manufofin kasa na yin rajistar katin SIM a watan Mayun 2021, Shugaba Buhari ya ce, “NIN zai rufe daya daga cikin raunin da ke tattare da tsarin tsaro. Za mu iya ganowa da sanin halayen ’yan Najeriya cikin sauƙi.

"Za mu gano mutane cikin sauki, gami da 'yan damfara."

Da yake tabbatar wa ‘yan Najeriya muhimmancin sabon tsarin, Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Digital, Isa Pantami, a watan Yunin 2021, ya yi ikirarin cewa al’amuran ta’addanci irinsu ‘yan fashi da garkuwa da mutane sun ragu matuka a cikin kasar sakamakon haka dagewar da gwamnati ta yi na mutane a Najeriya su yi rajistar NIN.

Comments

Popular posts from this blog

Bridging Digital Divides: Empowering People with Special Needs and Uniting Communities Through Technology

By Abdullahi Abdulhafiz Aliyu In today’s fast-changing digital landscape, access to technology is no longer a luxury—it is a necessity. Yet, for millions of Nigerians, especially people with special needs, the digital world remains out of reach due to systemic barriers and a lack of inclusive learning opportunities. My work as a journalist and digital advocate has focused on breaking these barriers, ensuring that technology serves as a tool for empowerment rather than exclusion. Through my engagement with individuals with disabilities and as the host of Duniyar Fasaha (Fasaha World) on Unity FM, I have worked to bridge the digital divide by providing foundational digital education to marginalized groups. By introducing people with special needs to basic computer skills such as Microsoft Word, Excel, PowerPoint, and internet navigation, I have witnessed firsthand how technology can unlock new opportunities and transform lives. Digital Skills for Special Needs: A Path to Inclusion Inclu...

Tragedy in Bukuru: Trader Killed, Two Injured in JMDB Task Force Operation

A tragic incident occurred in Bukuru, Jos South LGA, on Monday, resulting in the death of a trader, Nasiru Abubakar, and injuring two others. The incident happened during an enforcement operation by the Jos Metropolitan Development Board (JMDB) task force. The Nigerian Police Logo According to reports, the task force was attempting to disperse a group of criminal elements when a warning shot was fired, unfortunately hitting the trader. The incident also resulted in the destruction of several vehicles, with over five cars set ablaze. The Commissioner of Police, Emmanuel Adesina, promptly visited the scene to assess the situation, and normalcy has been restored. The police command has issued a stern warning to individuals with criminal intentions, urging them to desist from their activities or flee the state. 

Reps Approve Tinubu’s Emergency Rule Request for Rivers State

 The House of Representatives has approved President Bola Ahmed Tinubu’s request to impose a state of emergency in Rivers State following heightened political tensions and security concerns. The decision, made during a plenary session on Wednesday, comes after weeks of instability in the oil-rich state, where political clashes and reports of pipeline vandalism have raised national security concerns. Why the Emergency Rule? The crisis in Rivers State stems from an ongoing power tussle between Governor Siminalayi Fubara and state lawmakers, a situation that has escalated into widespread unrest. Reports also indicate that increased incidents of oil theft and pipeline vandalism are affecting Nigeria’s economic stability. President Tinubu, in his emergency rule proclamation, suspended Governor Fubara and other elected officials, appointing retired Vice Admiral Ibokette Ibas as the military administrator to oversee the state’s affairs. House of Representatives  Legislative Endor...