Skip to main content

IN KANA SON SANIN MATSAYIN APC A ZABEN 2023

 


Za a bude hada-hadar siyasa gadan-gadan ranar 28 ga watan Satumba 2022. Daga wannan rana hukumar zabe ta bada izini a shiga kamfen. Ba za a tsaya ba sai ranar 23 ga watan Fabrairu 2023, wato saura kwana biyu a fara zaben shugaban kasa dana yan majalisar dattijai da na tarayya.

In kana son sanin yadda mutanen Najeriya za su yi zabe kuma wa za su zaba ga hanyoyi da za ka yi duba da la'akari da su guda biyar.

Na Daya; 

Duba a Masallacin da kake sallar asuba, ko cocin da kake halarta, makotanka na gida a dama da hagu, gabas da yamma, shin zasu zabi APC, ko sauran jam'iyyun zasu zaba?

Na biyu;

Duba abokanka a kasuwa da wadanda kuke aiki tare a kamfanoni ko ofis dinku da wadanda kuke haduwa kullum wajen sana'a, mutum nawa ne zasu zabi APC, nawa ne zasu zabi sauran jam'iyyun?

Na uku;

Duba 'yan makarantarku ta Boko( wato jami'a da kolejojin ilimi da Polytechnics, masu yajin aiki da wadanda ke bakin aikinsu) da dalibai na zaure da majalisi islamiyya da duk gurin da kuke haduwa neman ilimi, mutum nawa ne zasu zabi jam'iyyar APC, nawa ne zasu zabi sauran jam'iyyun?

Na hudu;

Duba wadanda kuke mu'amala a filin wasa ko shakatawa da sharholiya, 'yan nishadi da yawo a duniya, su waye da waye a cikinsu zasu zabi APC, su waye kuma zasu zabi sauran jam'iyyun?

Na biyar;

Duba sosai a 'yan siyasar unguwarku a matakin cafta da mazaba da karamar hukuma da jiha har ma da kasa baki daya, su waye, suna iya tallan jam'iyyar APC ko sauran jam'iyyun?

Sakamakon da ka samu, shi ne hisabin da mutanen kasar nan suke kudirin aiwatar a ranar zabe. KAR KA YAUDARI KANKA

MALLAKIN RUBUTU BELLO MUHAMMAD SHARADA

Comments

Popular posts from this blog

Bridging Digital Divides: Empowering People with Special Needs and Uniting Communities Through Technology

By Abdullahi Abdulhafiz Aliyu In today’s fast-changing digital landscape, access to technology is no longer a luxury—it is a necessity. Yet, for millions of Nigerians, especially people with special needs, the digital world remains out of reach due to systemic barriers and a lack of inclusive learning opportunities. My work as a journalist and digital advocate has focused on breaking these barriers, ensuring that technology serves as a tool for empowerment rather than exclusion. Through my engagement with individuals with disabilities and as the host of Duniyar Fasaha (Fasaha World) on Unity FM, I have worked to bridge the digital divide by providing foundational digital education to marginalized groups. By introducing people with special needs to basic computer skills such as Microsoft Word, Excel, PowerPoint, and internet navigation, I have witnessed firsthand how technology can unlock new opportunities and transform lives. Digital Skills for Special Needs: A Path to Inclusion Inclu...

Yanzu yanzu: 'yan majalisar dattijai sun tafi hutu domin gudanar da yaƙin neman zaɓe

Majalisar dattijan Nigeria, sun tafi hutu a yau Laraba, domin samun cigaba da gudanar da harkokin yaƙin neman zaɓe a jam'iyyun da suke ciki, don tunkarar babban zaɓen shekarar 2023, kamar yadda shugaban majalisar, Sanata Ahmad Lawan, ya bayyana yayin zaman majalisar na wannan rana. Lawan yace zace zasu tafi hutun ne domin tabbatar da abubuwa sun zama cikin tsari a ƙasar nan, kuma za su dawo a ranar 28 ga watan Fabrairu, kwanaki uku kenan bayan an gudanar da zaɓen shugaban ƙasa dana yan majalisun tarayya, kafin su sake tafiya wani hutun a ranar 1 ga watan Maris, domin gudanar da zaɓen gwamnoni da yan majalisun dokokin jiha, da za'ayi a ranar 11 ga watan Maris. Cikin jawabinsa, Lawan yayi kira ga hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC, da kuma jami'an tsaro, akan su tabbatar sunyi ayyukansu yadda ya dace, domin yin zaɓe cikin kwanciyar hankali da lumana, karbabben zaɓe kuma sahihi. Majalisar Nigeriya

All Is Set For APC Presidential Primary.

All is now set for the All Progressives Congress (APC) Presidential primary in Abuja holding from Monday, June 6 to June 7 at the Eagle’s Square with six aspirants in the lead, Jasawa Times learned. The presidentail aspirant include the Vice-President Yemi Osibanjo; former Minister of Science and Technology, Ogbonnaya Onu, Ebonyi Gov. Dave Umahi; former Lagos Gov. Bola Ahmed Tinubu, former Minister of Transportation, Rotimi Amaechi and ex-Minister of State for Education, Chief Chukwuemeka Nwajiuba. The Eagles Square is expected to host about 2,240 delegates from the 36 states and the Federal Capital Territory. Expectedly, the influx of people into the FCT has increased, a development that has attracted more police presence at the Eagles Square and some hotels hosting the delegates and chieftains of the APC. Ahead of the event, the party’s National Chairman, Sen.Abdullahi Adamu on Sunday visited the Eagles Square where he expressed satisfaction with the facilities put in place by...