Skip to main content

Hukumar INEC tace ba ta da 'yan takarar Sanata a mazabun Yobe ta Arewa da Akwa Ibom ta Arewa maso Yamma daga APC

 Hukumar INEC tace ba ta da 'yan takarar Sanata a mazabun Yobe ta Arewa da Akwa Ibom ta Arewa maso Yamma daga APC




Har yanzu tsugene Bata karewa Sanata ahmad lawn da Kuma godswill akfabio ba, Domin kuwa Hukumar zabe mai zaman kanta a Najeriya, INEC, ta bayyana cewa Jam'iyya mai mulki a kasar, APC, ba ta da 'yan takarar Sanata a mazabun Yobe ta Arewa da Akwa Ibom ta Arewa maso Yamma.

Shugaban Majalisar Dattawan kasar, Ahmed Lawan, mai wakiltar Yobe ta Arewa na fafutukar samun tikitin tsayawa takara karkashin Jam'iyyar APC bayan da ya sha kaye a zaben fitar da gwani na dan takarar shugaban kasa

Hukumar zabe mai zaman kanta a Najeriya, INEC, ta bayyana cewa Jam'iyya mai mulki a kasar, APC, ba ta da 'yan takarar Sanata a mazabun Yobe ta Arewa da Akwa Ibom ta Arewa maso Yamma.

Shugaban Majalisar Dattawan kasar, Ahmed Lawan, mai wakiltar Yobe ta Arewa na fafutukar samun tikitin tsayawa takara karkashin Jam'iyyar APC bayan da ya sha kaye a zaben fitar da gwani na dan takarar shugaban kasa

Saidai Kwamishinan Hukumar zabe, Festus Okoye ya ce INEC ba ta da wani dan takarar APC da zai wakilci mazabun Yobe ta Arewa da Akwa Ibom ta Arewa maso Yamma.

A wata hira da Gidan Talabijin na Channels TV, Okoye ya kara da cewa "a mazabun biyu, an gabatar da sunayen mutum biyu kuma hukumar ta yanke hukuncin cewa mutanen ba su ne halastattun wadanda suka lashe zaben fitar da gwanin da APC ta gudanar ba kuma ba mu wallafa sunayensu ba".

Ya ce APC ta dora sunayen Lawan da Akpabio cikin jerin sunayen 'yan takara a shafin intanet na INEC amma hukumar zaben ta yanke hukuncin cewa mutanen biyu ba su ne aka tsayar da su ba a zaben fitar da gwanin Jam'iyyar.

A cewar Okoye, rashin wallafa sunayen mutanen biyu da bayanansu a karkashin mazabun na nufin zuw yanzu APC ba ta da sunayen 'yan takarar a mazabun biyu.

Ko a makon da ya gabata sai da INEC ta musanta sauya kwanan watan wasu takardu domin samun damar shigar da sunayen Lawan da Akpabio a matsayin 'yan takarar kujerar Sanata a babban zaben kasar na 2023.

INEC dai ta bayyana cewa ba ta wallafa foma-foman mutanen biyu ba - matakin da ya sa aka shigar da kara wadda kuma har yanzu take gaban alkali.

Hukumar zaben ta ce hakan ne ya sa ta yi watsi da duk wata dabara ta gabatar da takardun bogi da ke tabbatar da takarar mutanen biyu a daidai lokacin da maganar ke gaban kotu.

Comments

Popular posts from this blog

Bridging Digital Divides: Empowering People with Special Needs and Uniting Communities Through Technology

By Abdullahi Abdulhafiz Aliyu In today’s fast-changing digital landscape, access to technology is no longer a luxury—it is a necessity. Yet, for millions of Nigerians, especially people with special needs, the digital world remains out of reach due to systemic barriers and a lack of inclusive learning opportunities. My work as a journalist and digital advocate has focused on breaking these barriers, ensuring that technology serves as a tool for empowerment rather than exclusion. Through my engagement with individuals with disabilities and as the host of Duniyar Fasaha (Fasaha World) on Unity FM, I have worked to bridge the digital divide by providing foundational digital education to marginalized groups. By introducing people with special needs to basic computer skills such as Microsoft Word, Excel, PowerPoint, and internet navigation, I have witnessed firsthand how technology can unlock new opportunities and transform lives. Digital Skills for Special Needs: A Path to Inclusion Inclu...

Yanzu yanzu: 'yan majalisar dattijai sun tafi hutu domin gudanar da yaƙin neman zaɓe

Majalisar dattijan Nigeria, sun tafi hutu a yau Laraba, domin samun cigaba da gudanar da harkokin yaƙin neman zaɓe a jam'iyyun da suke ciki, don tunkarar babban zaɓen shekarar 2023, kamar yadda shugaban majalisar, Sanata Ahmad Lawan, ya bayyana yayin zaman majalisar na wannan rana. Lawan yace zace zasu tafi hutun ne domin tabbatar da abubuwa sun zama cikin tsari a ƙasar nan, kuma za su dawo a ranar 28 ga watan Fabrairu, kwanaki uku kenan bayan an gudanar da zaɓen shugaban ƙasa dana yan majalisun tarayya, kafin su sake tafiya wani hutun a ranar 1 ga watan Maris, domin gudanar da zaɓen gwamnoni da yan majalisun dokokin jiha, da za'ayi a ranar 11 ga watan Maris. Cikin jawabinsa, Lawan yayi kira ga hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC, da kuma jami'an tsaro, akan su tabbatar sunyi ayyukansu yadda ya dace, domin yin zaɓe cikin kwanciyar hankali da lumana, karbabben zaɓe kuma sahihi. Majalisar Nigeriya

All Is Set For APC Presidential Primary.

All is now set for the All Progressives Congress (APC) Presidential primary in Abuja holding from Monday, June 6 to June 7 at the Eagle’s Square with six aspirants in the lead, Jasawa Times learned. The presidentail aspirant include the Vice-President Yemi Osibanjo; former Minister of Science and Technology, Ogbonnaya Onu, Ebonyi Gov. Dave Umahi; former Lagos Gov. Bola Ahmed Tinubu, former Minister of Transportation, Rotimi Amaechi and ex-Minister of State for Education, Chief Chukwuemeka Nwajiuba. The Eagles Square is expected to host about 2,240 delegates from the 36 states and the Federal Capital Territory. Expectedly, the influx of people into the FCT has increased, a development that has attracted more police presence at the Eagles Square and some hotels hosting the delegates and chieftains of the APC. Ahead of the event, the party’s National Chairman, Sen.Abdullahi Adamu on Sunday visited the Eagles Square where he expressed satisfaction with the facilities put in place by...