Skip to main content

SHUGABANCIN MAJALISAR DATTIJAI


 BELLO MUHAMMAD SHARADA YA RUBUTA 


SHUGABANCIN MAJALISAR DATTIJAI


Ranar Talata mai zuwa wato 19 ga watan Yuli 2022, majalisar dattijai za ta koma bakin aiki. An yi hutun sallah. Zuwa ranar Lahadi 17 ga watan Yuli, duk wanda sunansa bai shiga cikin rumbum bayanai na masu takara ta shugaban kasa da mataimakansu da 'yan takara na majalisar dattijai da tarayya da INEC ta bude ba, an wuce gurin sai kuma in Allah ya kaimu kakar fidda 'yan takara na shekarar 2027.


'Yan majalisar dattijai masu ci guda 22 ne suka rasa takara, akasarinsu sun fito daga jam'iyyar APC. Wasu sun rasa kujerun ne sakamakon tafiya wata takarar, kamar shugaban majalisar dattijai Sanata Ahmad Ibrahim Lawan, wanda yake neman shugabanci na kasa da abokinsa Sanata Abdullahi Adamu ya kwadaita masa, wasu kuma saboda sun canza takarar kamar Sanata Sabo Nakudu ya je neman gwamna a Jigawa, wasu kuma saboda rikicin su da gwamnoni na jihohin su kamar Kano da Kebbi da Jigawa. Sabuwar majalisar dattijai da za a yi ta 10 in tsaffin gwamnoni suka kai labari a jihohin su a ZABUKAN 2023, za a samu tsaffin gwamnoni 28 a majalisar, yawansu ya karu daga mutum 14, sun ninka sau biyu.


Ganin an samu faduwar zabe a Primary Elections, da shugaban jam'iyya na APC na kasa Sanata Abdullah Adamu da Sanata Kashim Shettima wanda yanzu shi ne dan takarar mataimakin shugaban kasa na  jam'iyyar APC, Cif Bola Ahmed Tinubu, sun gana da shugaban kasa Muhammad Buhari gab da zai yi balaguro zuwa kasar Portugal a makon jiya, an yi zama domin warware matsalolin cikin gida na APC a majalisar dattijai amma, an tashi babu sakamako mai dadi da gamsarwa.


Daga ranar Talata zuwa Laraba da Alhamis bisa zance sahihi,  wasu da yawa cikin sanatoci zasu fice daga jam'iyyar APC su koma wasu jam'iyyu. A halin da ake ciki akwai sanatoci 61 na jam'iyyar APC da kuma 48 na sauran jam'iyyun da suka hada da PDP da NNPP da APGA da Labor Party da YPP. Idan sanatoci 13 suka fice daga jam'iyyar APC, Ahmad Lawan shugaban majalisar dattijai shi kuma alkiyamarsa ta siyasa ta tashi. Zai rasa shugabancin majalisar dattijai kuma zai iya rasa kujerarsa ta takara wacce a yanzu ma ba shi INEC ta karba ba, dama kuma ya zo na hudu ne a takarar shugabancin Najeriya na APC. Uku babu kenan. Haka siyasa take,  in kaine yau, gobe ba kai bane, wani ne. Wannan lissafin ya tabbata ba a samu canji, tunda harkar siyasa kamar sauyawar hawainiya yake.

In an samu wannan canjin mutum na farko da zai kwashi garabasa shi ne dan takarar shugabancin Najeriya na PDP Atiku Abubakar, mutum na biyu kuma da zai sharbi romo idan hakan ta kasance shi ne dan takarar shugabancin Najeriya a NNPP Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso. Wanda yake fuskantar babbar barazana kuma shi ne Bola Ahmed Adekunle Tinubu.

Shekarar zabe ta 2023 ta daban ce.

Comments

Popular posts from this blog

Bridging Digital Divides: Empowering People with Special Needs and Uniting Communities Through Technology

By Abdullahi Abdulhafiz Aliyu In today’s fast-changing digital landscape, access to technology is no longer a luxury—it is a necessity. Yet, for millions of Nigerians, especially people with special needs, the digital world remains out of reach due to systemic barriers and a lack of inclusive learning opportunities. My work as a journalist and digital advocate has focused on breaking these barriers, ensuring that technology serves as a tool for empowerment rather than exclusion. Through my engagement with individuals with disabilities and as the host of Duniyar Fasaha (Fasaha World) on Unity FM, I have worked to bridge the digital divide by providing foundational digital education to marginalized groups. By introducing people with special needs to basic computer skills such as Microsoft Word, Excel, PowerPoint, and internet navigation, I have witnessed firsthand how technology can unlock new opportunities and transform lives. Digital Skills for Special Needs: A Path to Inclusion Inclu...

Tragedy in Bukuru: Trader Killed, Two Injured in JMDB Task Force Operation

A tragic incident occurred in Bukuru, Jos South LGA, on Monday, resulting in the death of a trader, Nasiru Abubakar, and injuring two others. The incident happened during an enforcement operation by the Jos Metropolitan Development Board (JMDB) task force. The Nigerian Police Logo According to reports, the task force was attempting to disperse a group of criminal elements when a warning shot was fired, unfortunately hitting the trader. The incident also resulted in the destruction of several vehicles, with over five cars set ablaze. The Commissioner of Police, Emmanuel Adesina, promptly visited the scene to assess the situation, and normalcy has been restored. The police command has issued a stern warning to individuals with criminal intentions, urging them to desist from their activities or flee the state. 

Reps Approve Tinubu’s Emergency Rule Request for Rivers State

 The House of Representatives has approved President Bola Ahmed Tinubu’s request to impose a state of emergency in Rivers State following heightened political tensions and security concerns. The decision, made during a plenary session on Wednesday, comes after weeks of instability in the oil-rich state, where political clashes and reports of pipeline vandalism have raised national security concerns. Why the Emergency Rule? The crisis in Rivers State stems from an ongoing power tussle between Governor Siminalayi Fubara and state lawmakers, a situation that has escalated into widespread unrest. Reports also indicate that increased incidents of oil theft and pipeline vandalism are affecting Nigeria’s economic stability. President Tinubu, in his emergency rule proclamation, suspended Governor Fubara and other elected officials, appointing retired Vice Admiral Ibokette Ibas as the military administrator to oversee the state’s affairs. House of Representatives  Legislative Endor...