Skip to main content

SHUGABANCIN MAJALISAR DATTIJAI


 BELLO MUHAMMAD SHARADA YA RUBUTA 


SHUGABANCIN MAJALISAR DATTIJAI


Ranar Talata mai zuwa wato 19 ga watan Yuli 2022, majalisar dattijai za ta koma bakin aiki. An yi hutun sallah. Zuwa ranar Lahadi 17 ga watan Yuli, duk wanda sunansa bai shiga cikin rumbum bayanai na masu takara ta shugaban kasa da mataimakansu da 'yan takara na majalisar dattijai da tarayya da INEC ta bude ba, an wuce gurin sai kuma in Allah ya kaimu kakar fidda 'yan takara na shekarar 2027.


'Yan majalisar dattijai masu ci guda 22 ne suka rasa takara, akasarinsu sun fito daga jam'iyyar APC. Wasu sun rasa kujerun ne sakamakon tafiya wata takarar, kamar shugaban majalisar dattijai Sanata Ahmad Ibrahim Lawan, wanda yake neman shugabanci na kasa da abokinsa Sanata Abdullahi Adamu ya kwadaita masa, wasu kuma saboda sun canza takarar kamar Sanata Sabo Nakudu ya je neman gwamna a Jigawa, wasu kuma saboda rikicin su da gwamnoni na jihohin su kamar Kano da Kebbi da Jigawa. Sabuwar majalisar dattijai da za a yi ta 10 in tsaffin gwamnoni suka kai labari a jihohin su a ZABUKAN 2023, za a samu tsaffin gwamnoni 28 a majalisar, yawansu ya karu daga mutum 14, sun ninka sau biyu.


Ganin an samu faduwar zabe a Primary Elections, da shugaban jam'iyya na APC na kasa Sanata Abdullah Adamu da Sanata Kashim Shettima wanda yanzu shi ne dan takarar mataimakin shugaban kasa na  jam'iyyar APC, Cif Bola Ahmed Tinubu, sun gana da shugaban kasa Muhammad Buhari gab da zai yi balaguro zuwa kasar Portugal a makon jiya, an yi zama domin warware matsalolin cikin gida na APC a majalisar dattijai amma, an tashi babu sakamako mai dadi da gamsarwa.


Daga ranar Talata zuwa Laraba da Alhamis bisa zance sahihi,  wasu da yawa cikin sanatoci zasu fice daga jam'iyyar APC su koma wasu jam'iyyu. A halin da ake ciki akwai sanatoci 61 na jam'iyyar APC da kuma 48 na sauran jam'iyyun da suka hada da PDP da NNPP da APGA da Labor Party da YPP. Idan sanatoci 13 suka fice daga jam'iyyar APC, Ahmad Lawan shugaban majalisar dattijai shi kuma alkiyamarsa ta siyasa ta tashi. Zai rasa shugabancin majalisar dattijai kuma zai iya rasa kujerarsa ta takara wacce a yanzu ma ba shi INEC ta karba ba, dama kuma ya zo na hudu ne a takarar shugabancin Najeriya na APC. Uku babu kenan. Haka siyasa take,  in kaine yau, gobe ba kai bane, wani ne. Wannan lissafin ya tabbata ba a samu canji, tunda harkar siyasa kamar sauyawar hawainiya yake.

In an samu wannan canjin mutum na farko da zai kwashi garabasa shi ne dan takarar shugabancin Najeriya na PDP Atiku Abubakar, mutum na biyu kuma da zai sharbi romo idan hakan ta kasance shi ne dan takarar shugabancin Najeriya a NNPP Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso. Wanda yake fuskantar babbar barazana kuma shi ne Bola Ahmed Adekunle Tinubu.

Shekarar zabe ta 2023 ta daban ce.

Comments

Popular posts from this blog

Bridging Digital Divides: Empowering People with Special Needs and Uniting Communities Through Technology

By Abdullahi Abdulhafiz Aliyu In today’s fast-changing digital landscape, access to technology is no longer a luxury—it is a necessity. Yet, for millions of Nigerians, especially people with special needs, the digital world remains out of reach due to systemic barriers and a lack of inclusive learning opportunities. My work as a journalist and digital advocate has focused on breaking these barriers, ensuring that technology serves as a tool for empowerment rather than exclusion. Through my engagement with individuals with disabilities and as the host of Duniyar Fasaha (Fasaha World) on Unity FM, I have worked to bridge the digital divide by providing foundational digital education to marginalized groups. By introducing people with special needs to basic computer skills such as Microsoft Word, Excel, PowerPoint, and internet navigation, I have witnessed firsthand how technology can unlock new opportunities and transform lives. Digital Skills for Special Needs: A Path to Inclusion Inclu...

Yanzu yanzu: 'yan majalisar dattijai sun tafi hutu domin gudanar da yaƙin neman zaɓe

Majalisar dattijan Nigeria, sun tafi hutu a yau Laraba, domin samun cigaba da gudanar da harkokin yaƙin neman zaɓe a jam'iyyun da suke ciki, don tunkarar babban zaɓen shekarar 2023, kamar yadda shugaban majalisar, Sanata Ahmad Lawan, ya bayyana yayin zaman majalisar na wannan rana. Lawan yace zace zasu tafi hutun ne domin tabbatar da abubuwa sun zama cikin tsari a ƙasar nan, kuma za su dawo a ranar 28 ga watan Fabrairu, kwanaki uku kenan bayan an gudanar da zaɓen shugaban ƙasa dana yan majalisun tarayya, kafin su sake tafiya wani hutun a ranar 1 ga watan Maris, domin gudanar da zaɓen gwamnoni da yan majalisun dokokin jiha, da za'ayi a ranar 11 ga watan Maris. Cikin jawabinsa, Lawan yayi kira ga hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC, da kuma jami'an tsaro, akan su tabbatar sunyi ayyukansu yadda ya dace, domin yin zaɓe cikin kwanciyar hankali da lumana, karbabben zaɓe kuma sahihi. Majalisar Nigeriya

All Is Set For APC Presidential Primary.

All is now set for the All Progressives Congress (APC) Presidential primary in Abuja holding from Monday, June 6 to June 7 at the Eagle’s Square with six aspirants in the lead, Jasawa Times learned. The presidentail aspirant include the Vice-President Yemi Osibanjo; former Minister of Science and Technology, Ogbonnaya Onu, Ebonyi Gov. Dave Umahi; former Lagos Gov. Bola Ahmed Tinubu, former Minister of Transportation, Rotimi Amaechi and ex-Minister of State for Education, Chief Chukwuemeka Nwajiuba. The Eagles Square is expected to host about 2,240 delegates from the 36 states and the Federal Capital Territory. Expectedly, the influx of people into the FCT has increased, a development that has attracted more police presence at the Eagles Square and some hotels hosting the delegates and chieftains of the APC. Ahead of the event, the party’s National Chairman, Sen.Abdullahi Adamu on Sunday visited the Eagles Square where he expressed satisfaction with the facilities put in place by...