Skip to main content

SHUGABANCIN MAJALISAR DATTIJAI


 BELLO MUHAMMAD SHARADA YA RUBUTA 


SHUGABANCIN MAJALISAR DATTIJAI


Ranar Talata mai zuwa wato 19 ga watan Yuli 2022, majalisar dattijai za ta koma bakin aiki. An yi hutun sallah. Zuwa ranar Lahadi 17 ga watan Yuli, duk wanda sunansa bai shiga cikin rumbum bayanai na masu takara ta shugaban kasa da mataimakansu da 'yan takara na majalisar dattijai da tarayya da INEC ta bude ba, an wuce gurin sai kuma in Allah ya kaimu kakar fidda 'yan takara na shekarar 2027.


'Yan majalisar dattijai masu ci guda 22 ne suka rasa takara, akasarinsu sun fito daga jam'iyyar APC. Wasu sun rasa kujerun ne sakamakon tafiya wata takarar, kamar shugaban majalisar dattijai Sanata Ahmad Ibrahim Lawan, wanda yake neman shugabanci na kasa da abokinsa Sanata Abdullahi Adamu ya kwadaita masa, wasu kuma saboda sun canza takarar kamar Sanata Sabo Nakudu ya je neman gwamna a Jigawa, wasu kuma saboda rikicin su da gwamnoni na jihohin su kamar Kano da Kebbi da Jigawa. Sabuwar majalisar dattijai da za a yi ta 10 in tsaffin gwamnoni suka kai labari a jihohin su a ZABUKAN 2023, za a samu tsaffin gwamnoni 28 a majalisar, yawansu ya karu daga mutum 14, sun ninka sau biyu.


Ganin an samu faduwar zabe a Primary Elections, da shugaban jam'iyya na APC na kasa Sanata Abdullah Adamu da Sanata Kashim Shettima wanda yanzu shi ne dan takarar mataimakin shugaban kasa na  jam'iyyar APC, Cif Bola Ahmed Tinubu, sun gana da shugaban kasa Muhammad Buhari gab da zai yi balaguro zuwa kasar Portugal a makon jiya, an yi zama domin warware matsalolin cikin gida na APC a majalisar dattijai amma, an tashi babu sakamako mai dadi da gamsarwa.


Daga ranar Talata zuwa Laraba da Alhamis bisa zance sahihi,  wasu da yawa cikin sanatoci zasu fice daga jam'iyyar APC su koma wasu jam'iyyu. A halin da ake ciki akwai sanatoci 61 na jam'iyyar APC da kuma 48 na sauran jam'iyyun da suka hada da PDP da NNPP da APGA da Labor Party da YPP. Idan sanatoci 13 suka fice daga jam'iyyar APC, Ahmad Lawan shugaban majalisar dattijai shi kuma alkiyamarsa ta siyasa ta tashi. Zai rasa shugabancin majalisar dattijai kuma zai iya rasa kujerarsa ta takara wacce a yanzu ma ba shi INEC ta karba ba, dama kuma ya zo na hudu ne a takarar shugabancin Najeriya na APC. Uku babu kenan. Haka siyasa take,  in kaine yau, gobe ba kai bane, wani ne. Wannan lissafin ya tabbata ba a samu canji, tunda harkar siyasa kamar sauyawar hawainiya yake.

In an samu wannan canjin mutum na farko da zai kwashi garabasa shi ne dan takarar shugabancin Najeriya na PDP Atiku Abubakar, mutum na biyu kuma da zai sharbi romo idan hakan ta kasance shi ne dan takarar shugabancin Najeriya a NNPP Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso. Wanda yake fuskantar babbar barazana kuma shi ne Bola Ahmed Adekunle Tinubu.

Shekarar zabe ta 2023 ta daban ce.

Comments

Popular posts from this blog

All Is Set For APC Presidential Primary.

All is now set for the All Progressives Congress (APC) Presidential primary in Abuja holding from Monday, June 6 to June 7 at the Eagle’s Square with six aspirants in the lead, Jasawa Times learned. The presidentail aspirant include the Vice-President Yemi Osibanjo; former Minister of Science and Technology, Ogbonnaya Onu, Ebonyi Gov. Dave Umahi; former Lagos Gov. Bola Ahmed Tinubu, former Minister of Transportation, Rotimi Amaechi and ex-Minister of State for Education, Chief Chukwuemeka Nwajiuba. The Eagles Square is expected to host about 2,240 delegates from the 36 states and the Federal Capital Territory. Expectedly, the influx of people into the FCT has increased, a development that has attracted more police presence at the Eagles Square and some hotels hosting the delegates and chieftains of the APC. Ahead of the event, the party’s National Chairman, Sen.Abdullahi Adamu on Sunday visited the Eagles Square where he expressed satisfaction with the facilities put in place by...

2023 ELECTION: BVAS mock accreditation Feb 4… INEC

The Independent National Electoral Commission (INEC) has said that it would conduct a mock accreditation of registered voters in 436 polling units (PUs) nationwide, on February 4 using its Bimodal Voter Accreditation System (BVAS) machines. The INEC Chairman, Prof. Mahmood Yakubu, said this during a meeting with Resident Electoral Commissioners (RECs) on Friday in Abuja. He said that 436 Bimodal Voter Accreditation System (BVAS) machines would be deployed for the exercise. “As you are already aware, the commission has taken delivery of the BVAS machines for the election. We have also dutifully tested each machine in our offices nationwide to ensure its functionality. “The next step is to conduct field tests across the country involving actual voters. For this reason, and in readiness for nationwide deployment, the commission is conducting a mock accreditation of voters similar to what was done ahead of the recent Ekiti and Osun states governorship elections. “The mock accreditation wil...

Concern PDP Muslim Youth Council paid a courtesy visit to Plateau State Governor-elect.

A coalition Muslim PDP Youth in Plateau state called Concern PDP Muslim Youth Council paid a congratulatory visit to Plateau Satet Governor-elect Barrister Caleb Mutgwang. Leading the delegation Hon. Kabiru Garkuwa, while delivering the Goodwill message  stated that the Council embarked on the visit to thank the Governor and show their unwavering faith and support for the victory at the recently concluded election. In his speech, Garkuwa, “Praised God for the glorious victory achieved by our dear Party PDP in general elections”  He also Added that, “with the like of his Excellency's at the helm of affairs in governance, Plateau State will be in safe hands”. He as well commended the commitments and the sacrifices of Hon. Yary Kumci, appreciated his kind support and benevolence always accorded to the group.  Garkuwa while presenting a letter to Governor elect.  Garkuwa also appreciate other officials among are   Hajiya Jamila Gwandu, Alh. Aminu Abdullahi (Jos...