Skip to main content

KALUBALE DA BARAZANAR DA FANNIN KIWON LAFIYA KE FUSKANTA

 Daga 'Ya'yanta; Shawara Ta ZUWA GA GWAMNATI DA HUKUMOMI MASU RUWA DA TSAKI A BANGAREN AIKIN ASIBITI.


Daga Nasir Yusuf Jibril, Yola

Kamar yadda muka sani, majalisar ma'aikata masu kula da majinyata ta duniya (International  Council Of Nurses) ta ayyana, ranar shida zuwa sha biyu ga watan mayu (6-12 May)  na kowace shekara a matsayin ranar ma'aikata masu kula da majinyata (International Nurses Day), zan yi amfani da wannan dama inyi tsokaci da kuma ƙara jawo hankalin hukumomi da gwamnati kan  irin hali da dabi'u da ma'aikata masu kula da majinyata da sauran ma'aikatan asibiti ke nunawa na rashin kwarewa da rashin  sanin makaman aiki (Law and Ethics) akan mu'amalar su da majinyata da kuma masu jiran majinyata, musamman a jihar Adamawa, inda  korafe-korafe yayi yawa kan yadda ma'aikatan asibiti ke nuna mummunar mu'amala na rashin ganin darajar mutane yayin aiki.

 Ina amfani da wannan dama wajen jawo hankalin Majalisar ma'aikatan kula da jinya da ungozoma(Nursing and Midwives Council Of Nigeria), da kuma kungiyar  gamayyar ma'aikatan kiwon lafya wato (Joint Health Sector Union), gwamnati, da sauran kungiyoyi masu ruwa da tsaki a bangaren kiwon lafiya.

Da farko dai, sanin kanmu ne cewa kowani fage na aiki na da ka'idoji da dabi'u na yin sa, wato (Law and Ethics). Ita ma wannan fage naku ba a barta kara zube ba, tana da nata dokoki da ka'idojin aiki. 

Koke-koke sun yi yawa akan ma'aikatan asibiti musamman ma “nurses" da “midwives", wajen nuna mummunar mu'amala tsakanin su da majinyata da kuma masu jiran mai jinya.

Kusan yanxu idan ka kira sunan “nurse” a cikin mutane, babban ma'anar da zai fara zuwa ransu shi ne; rashin kunya, mummunar mu'amala, girman kai da sauran dabi'u na walakanci.

A nawa mahangar wannan mummunar mu'amala da ma'aikatan asibiti ke nunawa, tabbaci ne na rashin kwarewa da rashin sanin makaman aiki, sannan kuma tabbaci ne na rashin ma faɗi ko in ce sakacin masu faɗa aji ne a wannan fage, inda hakan ya janyo zubewar mutuncin ma'aikatan asibiti a idon mutane da dama, ya Kum sa a maimakon mu dinga ganin su a matsayin masu tausayi da ceto rayuwar al'umma, mun koma ganin su a matsayin masu nuna rashin tausayi da hallaka al'umma.




A makon Jiya,  saura kadan na sharara wa wata “nurse" mari a sakamakon nuna rashin ɗa'a da ganin darajar dan Adam. Ba komai ya jawo haka ba sai rashin bin  ka'idoji da kuma dokokin aiki (Law and Ethics) wanda ya janyo wa aikin baƙin jini da kuma mummunar fassara.

Bugu da kari, akwai wani ƙalubale ko in ce  matsalar da take kara tinkaro fannin kiwon lafiyar mu, musamman mu nan Adamawa.
Wannan matsalar kuwa ita ce; fara yawaitar Makarantantu koyon harkar lafiya masu zaman kansu wanda ba a  tantance su ba a hukuman ce  ko in ce ba a gama tantance su ba a hukuman ce (un-acreditate private colleges of health...)
Yawan cin wayan nan makarantun  din dalibai marasa kwarewa (quacks)  kawai ake fitar wa...!
Domin galibin daliban Korarrun daliban kolejin horar da ma'aikatan jinya ta jihar Adamawa ne(nursing school, Yola.) ko makarantar koyon aikin lafiya( school of health) da ke mubi, suke dawowa nan.
Wanda a bayya ne ya ke  an san wa 'yan can makarantun sun ginu ne kawai domin kasuwanci ba don inganta bangaren kiwon lafiya ba.
Don haka zaka tarar basa iya daukan kwararru wanda suka dade kuma suka samu gogewa a fan nin,  domin baza su iya cire kudi su biya su yadda ya kamata ba, sai dai su dauko 'yan bana bakwai wanda kudi kadan zasu musu aiki.
Wannan dalili yasa cin hanci da alfarma ya shigo cikin harkar, inda ya kara   nuna rashin kwarewan irin wa yan nan daliban a waje koyon san makaman aiki ( I.T)  har ma bayan kammalawar su 
 Don haka  laifin irin wayan nan daliban shi ke shafan kwararrun...!
 jama'a kuma suke yin musu  kudin goro...
A takaice dai abunda nake son fadi a nan shi ne; Makarantun kiwon lafiya masu zaman kansu da ( Private schools of health)  da su ke ta fitowa a Adamawa gaskiya ba alkhairi ba ne ga fanin kiwon lafiyar jihar, hasali sai dai a ce barazana ne ga fan nin.

Shawara ta zuwa ga kungiyoyi da hukumomi masu ruwa da tsaki kan harkar kiwon lafiya shi ne; Dalibai da ake yayewa musamman 'yan kolejin horar da ma'aikatan jinya (college of nursing) don matsalar tafi yawa daga wajen su, Ya kamata a saka musu darussan koyon sanin ka'idoji da dokokin aiki (Law and Ethics) tun daga ajin farko har zuwa ajin karshe, sannan kuma a musu jarabawa ta musamman akai.

 Gwamnati da hukumomin kiwon lafiya su yalwata ofisoshin karban korafe-korafe na majinyata da masu jiran su, kan mu'amalar su da ma'aikatan asibiti. Kungiyoyi na kiwon lafiya musamman kungiyar “nursing and midwives”   da sauran kungiyoyi masu ruwa da tsaki a bangaren kiwon lafiya, su dinga haɗa taron wayarwa al'umma kai game da ƴancin su da hakkokin su a kan ma'aikatan asibiti da ma asibiti baki ɗaya (na gwamnati da masu zaman kansu) musamman a irin wannan lokaci na bikin murnar satin  ma'aikatan jinya  wato (Nurses week).

Majalisar ma'aikatan jinya da ungozoma, wato (Nursing and Midwifery Council of Nigeria) ta dinga daukan mataki da ya dace a duk lokacin da ta samu rahoton taka dokokin aiki komai ƙanƙantar sa. 

Yakamata hukumomi  masu ruwa da tsaki da gwamnati su dai na bada lasisi ga  makarantun da basu dace ba,  idan ya kama dole toh sai a  tabbatar da inganci su, kuma a sa musu ido kan dokokin da aka saka musu. Son samu ya zamanto gwamnati ne kawai ke da alhakin kafa makarantun kiwon lafiya.
Ina ga zai fi musu saukin kula, saɓanin idan sunyi yawa...!!!

Hausawa sun ce da haihuwar goma marasa amfani gara haihuwar daya mai amfani.
Kamar yadda gwamnati, ita kadai ke kula da harkokin da ya shafi tsaro da jami'an tsaro, ba tare da ta bawa wata ko wani mai zaman kan shi  damar mallakar police ko soja ba, domin muhimmancin bangaren, haka muke fata suyi dokan hana mallakar makarantun kiwon lafiya ga Mutane ko in ce 'yan kasuwa masu zaman kansu, musamman a jihar mu da kasa ma baki daya, don samun daman baiwa bangaren kulawa yadda ya kamata.

Idan har aka karfafa waɗannan dokokin, to  za'a samu daidaito akan wannan matsalar da muke fama da ita, don kowa zai tsaya a iyakarsa .

Allah ya kara rufa man asiri. Allah ya bai wa ma'aikatan lafiyar mu juriya, basira, da kuma jajircewa kan aikinsu. Marasa lafiyar mu, Allah ya basu lfya.

Wassalam.

Nasir Yusuf Jibril, Yola.
Daga jami'ar Bayero, Kano, Tsangayar sadarwa, sashen koyon makaman aikin jarida.

Comments

Popular posts from this blog

NGF Promises Improved Minimum Wage Amid Ongoing Negotiations

The Nigeria Governors' Forum (NGF) has assured Nigerians and organized labor that negotiations are underway to establish a better minimum wage. This comes after the governors previously rejected the Federal Government's proposal of N62,000, citing that some states would need to borrow to pay salaries. Despite this, organized labor continues to push for a wage of N250,000. Nigeria Governor's Forum  Following the Federal Executive Council's postponement of the minimum wage discussion, the governors held an emergency meeting, which extended into the early hours of Thursday. According to a communiqué signed by NGF acting Director, Media, Ahmed Salihu, the forum discussed various national issues, including the new national minimum wage. The governors agreed to continue engaging with key stakeholders to reach a mutually acceptable solution, assuring that better wages will result from the ongoing negotiations. They also discussed the World Bank-Nigeria for Women Project Scale-

JUST NOW: Woman Caught with Stolen AK-47

Security forces apprehended a middle-aged woman, Aisha Abubakar, from Katsina State, while she was on a bus traveling to Abuja from Katsina. The woman was found in possession of a stolen AK-47 rifle, prompting her arrest. Suspected Aisha Abubakar  During interrogation, Aisha revealed that she was driven by extreme hunger and desperation to accept the task from unknown individuals. She claimed that she was instructed to transport the weapon to a designated location near Yantumaki, where the owners would retrieve it. Aisha maintained that this was her first involvement in such a dangerous and illegal activity, and that her dire circumstances left her with little choice but to accept the job. Her statement highlights the devastating impact of poverty and hunger on individuals, leading them to engage in illicit activities out of desperation.

Tragedy at the National Assembly: Customs Officer Passes Away

Tragedy struck at the National Assembly on Tuesday when a senior officer of the Nigeria Customs Service passed away during a meeting with a House Committee. According to a statement released by House Spokesman Akin Rotimi, the officer suddenly fell ill at approximately 1 pm and despite prompt medical attention from first responders and the National Assembly Clinic's medical team, sadly succumbed to his condition. Nass Out of respect for the family's privacy, the officer's identity has not been disclosed at this time. The House of Representatives extends its heartfelt condolences to the family, friends, and colleagues of the deceased and stands ready to support investigations into the circumstances surrounding the incident.