Skip to main content

SSANU da NASU sun dakatar da yajin aiki zuwa watanni biyu

 



Kwamitin haɗin gwiwa na ƙungiyar manyan ma’aikatan jami’o’in Najeriya (SSANU) da na ƙungiyoyin ma’aikata sashen da ba koyarwa ba (NASU) sun dakatar da yajin aikin da suke yi na tsawon watanni biyu.

Wani mamba a kungiyar haɗin gwiwar kuma shugaban SSANU na ƙasa, Mohammed Ibrahim ne ya bayyana hakan a wata hira da jaridar The Nation ta wayar tarho ranar Asabar a Abuja.

Ya ce dakatarwar za ta fara aiki ne daga ranar Larabar mako mai zuwa. “Eh, mun dakatar da yajin aikin na tsawon watanni biyu,” in ji shugaban SSANU.

A cewar Ibrahim, gwamnatin tarayya ta ware naira biliyan 50 domin biyan alawus-alawus ga mambobin SSANU, NASU da kuma ƙungiyar malaman jami’o’i ta ASUU.

Ya kuma ce ƙungiyoyin sun cim ma yarjejeniya da gwamnati kan sharuɗɗan dawowa bakin aikinsu da fatan za a aiwatar da yarjejeniyar cikin watanni biyu.

Yajin aikin da SSANU da NASU suka yi, ya sa aka dakatar da bayar da takardun shedar kammala karatu, da kuma gudanar al’amuran sa suka shafi tafiya aikin hidimar ƙasa na NYSC.

A wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar, shugaban SSANU ya ce: “A yau, bayan tattaunawa da mai girma ministan ilimi da kuma gamsuwar da muka cewa gwamnati a wannan karon za ta jajirce wajen amincewa da mutunta yarjejeniyoyin da aka cim ma a tarurrukan da aka yi, muna sanar da ku wata tazarar watanni biyu da muka bai wa gwamnati don aiwatar da yarjejeniyar da aka cim ma.

“Burinmu ne, ganin irin tabbacin da mai girma ministan ilimi ya yi da kuma jajircewarmu na ganin an kawo karshen rikicin da ke faruwa, cewa damar da za a samu na watanni biyu zai isa a ɗauki matakan da za su kawo ƙarshen saɓanin gaba daya”

Comments

Popular posts from this blog

Bridging Digital Divides: Empowering People with Special Needs and Uniting Communities Through Technology

By Abdullahi Abdulhafiz Aliyu In today’s fast-changing digital landscape, access to technology is no longer a luxury—it is a necessity. Yet, for millions of Nigerians, especially people with special needs, the digital world remains out of reach due to systemic barriers and a lack of inclusive learning opportunities. My work as a journalist and digital advocate has focused on breaking these barriers, ensuring that technology serves as a tool for empowerment rather than exclusion. Through my engagement with individuals with disabilities and as the host of Duniyar Fasaha (Fasaha World) on Unity FM, I have worked to bridge the digital divide by providing foundational digital education to marginalized groups. By introducing people with special needs to basic computer skills such as Microsoft Word, Excel, PowerPoint, and internet navigation, I have witnessed firsthand how technology can unlock new opportunities and transform lives. Digital Skills for Special Needs: A Path to Inclusion Inclu...

Tragedy in Bukuru: Trader Killed, Two Injured in JMDB Task Force Operation

A tragic incident occurred in Bukuru, Jos South LGA, on Monday, resulting in the death of a trader, Nasiru Abubakar, and injuring two others. The incident happened during an enforcement operation by the Jos Metropolitan Development Board (JMDB) task force. The Nigerian Police Logo According to reports, the task force was attempting to disperse a group of criminal elements when a warning shot was fired, unfortunately hitting the trader. The incident also resulted in the destruction of several vehicles, with over five cars set ablaze. The Commissioner of Police, Emmanuel Adesina, promptly visited the scene to assess the situation, and normalcy has been restored. The police command has issued a stern warning to individuals with criminal intentions, urging them to desist from their activities or flee the state. 

All Is Set For APC Presidential Primary.

All is now set for the All Progressives Congress (APC) Presidential primary in Abuja holding from Monday, June 6 to June 7 at the Eagle’s Square with six aspirants in the lead, Jasawa Times learned. The presidentail aspirant include the Vice-President Yemi Osibanjo; former Minister of Science and Technology, Ogbonnaya Onu, Ebonyi Gov. Dave Umahi; former Lagos Gov. Bola Ahmed Tinubu, former Minister of Transportation, Rotimi Amaechi and ex-Minister of State for Education, Chief Chukwuemeka Nwajiuba. The Eagles Square is expected to host about 2,240 delegates from the 36 states and the Federal Capital Territory. Expectedly, the influx of people into the FCT has increased, a development that has attracted more police presence at the Eagles Square and some hotels hosting the delegates and chieftains of the APC. Ahead of the event, the party’s National Chairman, Sen.Abdullahi Adamu on Sunday visited the Eagles Square where he expressed satisfaction with the facilities put in place by...