Skip to main content

SSANU da NASU sun dakatar da yajin aiki zuwa watanni biyu

 



Kwamitin haɗin gwiwa na ƙungiyar manyan ma’aikatan jami’o’in Najeriya (SSANU) da na ƙungiyoyin ma’aikata sashen da ba koyarwa ba (NASU) sun dakatar da yajin aikin da suke yi na tsawon watanni biyu.

Wani mamba a kungiyar haɗin gwiwar kuma shugaban SSANU na ƙasa, Mohammed Ibrahim ne ya bayyana hakan a wata hira da jaridar The Nation ta wayar tarho ranar Asabar a Abuja.

Ya ce dakatarwar za ta fara aiki ne daga ranar Larabar mako mai zuwa. “Eh, mun dakatar da yajin aikin na tsawon watanni biyu,” in ji shugaban SSANU.

A cewar Ibrahim, gwamnatin tarayya ta ware naira biliyan 50 domin biyan alawus-alawus ga mambobin SSANU, NASU da kuma ƙungiyar malaman jami’o’i ta ASUU.

Ya kuma ce ƙungiyoyin sun cim ma yarjejeniya da gwamnati kan sharuɗɗan dawowa bakin aikinsu da fatan za a aiwatar da yarjejeniyar cikin watanni biyu.

Yajin aikin da SSANU da NASU suka yi, ya sa aka dakatar da bayar da takardun shedar kammala karatu, da kuma gudanar al’amuran sa suka shafi tafiya aikin hidimar ƙasa na NYSC.

A wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar, shugaban SSANU ya ce: “A yau, bayan tattaunawa da mai girma ministan ilimi da kuma gamsuwar da muka cewa gwamnati a wannan karon za ta jajirce wajen amincewa da mutunta yarjejeniyoyin da aka cim ma a tarurrukan da aka yi, muna sanar da ku wata tazarar watanni biyu da muka bai wa gwamnati don aiwatar da yarjejeniyar da aka cim ma.

“Burinmu ne, ganin irin tabbacin da mai girma ministan ilimi ya yi da kuma jajircewarmu na ganin an kawo karshen rikicin da ke faruwa, cewa damar da za a samu na watanni biyu zai isa a ɗauki matakan da za su kawo ƙarshen saɓanin gaba daya”

Comments

Popular posts from this blog

NGF Promises Improved Minimum Wage Amid Ongoing Negotiations

The Nigeria Governors' Forum (NGF) has assured Nigerians and organized labor that negotiations are underway to establish a better minimum wage. This comes after the governors previously rejected the Federal Government's proposal of N62,000, citing that some states would need to borrow to pay salaries. Despite this, organized labor continues to push for a wage of N250,000. Nigeria Governor's Forum  Following the Federal Executive Council's postponement of the minimum wage discussion, the governors held an emergency meeting, which extended into the early hours of Thursday. According to a communiqué signed by NGF acting Director, Media, Ahmed Salihu, the forum discussed various national issues, including the new national minimum wage. The governors agreed to continue engaging with key stakeholders to reach a mutually acceptable solution, assuring that better wages will result from the ongoing negotiations. They also discussed the World Bank-Nigeria for Women Project Scale-...

Bridging Digital Divides: Empowering People with Special Needs and Uniting Communities Through Technology

By Abdullahi Abdulhafiz Aliyu In today’s fast-changing digital landscape, access to technology is no longer a luxury—it is a necessity. Yet, for millions of Nigerians, especially people with special needs, the digital world remains out of reach due to systemic barriers and a lack of inclusive learning opportunities. My work as a journalist and digital advocate has focused on breaking these barriers, ensuring that technology serves as a tool for empowerment rather than exclusion. Through my engagement with individuals with disabilities and as the host of Duniyar Fasaha (Fasaha World) on Unity FM, I have worked to bridge the digital divide by providing foundational digital education to marginalized groups. By introducing people with special needs to basic computer skills such as Microsoft Word, Excel, PowerPoint, and internet navigation, I have witnessed firsthand how technology can unlock new opportunities and transform lives. Digital Skills for Special Needs: A Path to Inclusion Inclu...

Tragedy at the National Assembly: Customs Officer Passes Away

Tragedy struck at the National Assembly on Tuesday when a senior officer of the Nigeria Customs Service passed away during a meeting with a House Committee. According to a statement released by House Spokesman Akin Rotimi, the officer suddenly fell ill at approximately 1 pm and despite prompt medical attention from first responders and the National Assembly Clinic's medical team, sadly succumbed to his condition. Nass Out of respect for the family's privacy, the officer's identity has not been disclosed at this time. The House of Representatives extends its heartfelt condolences to the family, friends, and colleagues of the deceased and stands ready to support investigations into the circumstances surrounding the incident.