Skip to main content

AN BUKACI IYAYE SU JI TSORON ALLAH WAJEN SAUKE NAUYIN TARBIYA DA A KA DAURA MUSA

 


An yi kira ga iyaye su ji tsoron Allah wajen sauke nauyin da Allah Ya daura mu su na tarbiyantar da ‘ya‘yayen su yadda ya kamata. 

Kazalika an shawarce su da su rika mayar da hankali akan harkokin yaran na yau da kullum don gujewa jefa su halin ni ‘ya su.

Mai Unguwar Rogo/Layin Dan Badawai dake nan birnin Jos din jihar Pilato, Alhaji Aliyu Muhammad Dan Badawai ne yayi wannan Kira ranar Asabar, a wajen taron yaye dalibai na shekara-shekara da Makarantar Skyline ta shirya a nan cikin garin Jos.

Mai Unguwa Dan Badawai daya kasance bako mai jawabi a wajen taron, ya tunatar da al'umma cewa, Allah Ya halicce su ne don su bautata Mishi, yana mai cewa, ta hanyar neman ilimi ne  mutum zai san hanyoyin dazai bi wajen bautatawa.

A lokacin da yake Jan hankalin iyaye da suke nuna halin ko inkula akan karatun ‘ya‘yan Su, Alhaji Aliyu Dan Badawai ya shawarcesu dasu tuna da yadda haduwar Su da Ubangiji zata kasance, domin kuwa a cewar Shi, za'a tambayi kowa akan kiwon da aka bashi.

Game da halin tsadar rayuwa da ake ciki kuwa, Alhaji Danbadawai ya shawarci al'umma suyi hakuri da wannan jarabawa don samun dacewar Ubangiji.

A nashi tsokacin mu'assashin Skyline, Malam Ahmad Abubakar Ahmad, ya bukaci iyaye da su cigaba da bayar da hadin Kai wajen ilimantar musu da Yara, ya na mai Mika godiyar shi wa mahalarts taron abisa amsa gayyatar da ka yi mu Su.

Jasawa times ta rawaito cewa, kansilan Anguwan Rogo/Rimi/ Sabon Layi, wato Honourable Sulaiman Sultan ta bakin Wakilan Shi, ya jaddada muhimmancin baiwa Yara tarbiya don kaucewa jefasu kan mummunar hanya.

Comments

Popular posts from this blog

Bridging Digital Divides: Empowering People with Special Needs and Uniting Communities Through Technology

By Abdullahi Abdulhafiz Aliyu In today’s fast-changing digital landscape, access to technology is no longer a luxury—it is a necessity. Yet, for millions of Nigerians, especially people with special needs, the digital world remains out of reach due to systemic barriers and a lack of inclusive learning opportunities. My work as a journalist and digital advocate has focused on breaking these barriers, ensuring that technology serves as a tool for empowerment rather than exclusion. Through my engagement with individuals with disabilities and as the host of Duniyar Fasaha (Fasaha World) on Unity FM, I have worked to bridge the digital divide by providing foundational digital education to marginalized groups. By introducing people with special needs to basic computer skills such as Microsoft Word, Excel, PowerPoint, and internet navigation, I have witnessed firsthand how technology can unlock new opportunities and transform lives. Digital Skills for Special Needs: A Path to Inclusion Inclu...

Yanzu yanzu: 'yan majalisar dattijai sun tafi hutu domin gudanar da yaƙin neman zaɓe

Majalisar dattijan Nigeria, sun tafi hutu a yau Laraba, domin samun cigaba da gudanar da harkokin yaƙin neman zaɓe a jam'iyyun da suke ciki, don tunkarar babban zaɓen shekarar 2023, kamar yadda shugaban majalisar, Sanata Ahmad Lawan, ya bayyana yayin zaman majalisar na wannan rana. Lawan yace zace zasu tafi hutun ne domin tabbatar da abubuwa sun zama cikin tsari a ƙasar nan, kuma za su dawo a ranar 28 ga watan Fabrairu, kwanaki uku kenan bayan an gudanar da zaɓen shugaban ƙasa dana yan majalisun tarayya, kafin su sake tafiya wani hutun a ranar 1 ga watan Maris, domin gudanar da zaɓen gwamnoni da yan majalisun dokokin jiha, da za'ayi a ranar 11 ga watan Maris. Cikin jawabinsa, Lawan yayi kira ga hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC, da kuma jami'an tsaro, akan su tabbatar sunyi ayyukansu yadda ya dace, domin yin zaɓe cikin kwanciyar hankali da lumana, karbabben zaɓe kuma sahihi. Majalisar Nigeriya

All Is Set For APC Presidential Primary.

All is now set for the All Progressives Congress (APC) Presidential primary in Abuja holding from Monday, June 6 to June 7 at the Eagle’s Square with six aspirants in the lead, Jasawa Times learned. The presidentail aspirant include the Vice-President Yemi Osibanjo; former Minister of Science and Technology, Ogbonnaya Onu, Ebonyi Gov. Dave Umahi; former Lagos Gov. Bola Ahmed Tinubu, former Minister of Transportation, Rotimi Amaechi and ex-Minister of State for Education, Chief Chukwuemeka Nwajiuba. The Eagles Square is expected to host about 2,240 delegates from the 36 states and the Federal Capital Territory. Expectedly, the influx of people into the FCT has increased, a development that has attracted more police presence at the Eagles Square and some hotels hosting the delegates and chieftains of the APC. Ahead of the event, the party’s National Chairman, Sen.Abdullahi Adamu on Sunday visited the Eagles Square where he expressed satisfaction with the facilities put in place by...