Skip to main content

Gwamnatin Jihar Plateau ta haramtawa kungiyar Kwadago zanga-zanga a jihar

 



Daga Mubarak Sani

Gwamnatin Jihar Plateau ta haramtawa kungiyar Kwadago zanga-zangar gama gari da take shirin yi gobe Talata a fadin kasar.

Sanarwar da ta fito daga fadar Gwamnatin jihar a yammacin yau litinin 25, ga watan Yulin 2022 ta bayyana cewa Gwamnatin jihar ta samu labarin shirin zanga-zangar inda tace baza ta amince da ita ba.

Gwamnatin ta bayyana cewa tana sane da dokar da ta bawa ma'aikata damar gudanar da zanga-zanga amma saidai har yanzu Jihar bata gama murmurewa ba daga tashe tashen hankula. Bugu da kari dama akwai dokar da aka sanya a baya wacce ta haramta duk wata irin zanga-zanga a fadin jihar kuma har yanzu ta nan.

Sanarwar ta kara da cewa kungiyar tayi gaggawar janye zanga-zangar domin baza a bari wasu bata gari suyi angulu da kan zabo ba domin bata zaman lafiyar da aka samu.

Daga karshe, Gwamnatin tace ta baza jami'an tsaro lungu da sako na fadin jihar domin tabbatar da doka da oda tare da hukunta duk wanda aka gani da sunan zanga-zanga.

Idan ba a manta ba dai, kungiyar Kwadagon ta NLC a makon daya gabata ta fitar da sanarwar gayyata ga rassanta na fadin kasar domin goyawa kungiyar malaman jami'a baya saboda kawo karshen yajin aikin da aka kwashe sama da watanni biyar anayi.

Comments

Popular posts from this blog

Bridging Digital Divides: Empowering People with Special Needs and Uniting Communities Through Technology

By Abdullahi Abdulhafiz Aliyu In today’s fast-changing digital landscape, access to technology is no longer a luxury—it is a necessity. Yet, for millions of Nigerians, especially people with special needs, the digital world remains out of reach due to systemic barriers and a lack of inclusive learning opportunities. My work as a journalist and digital advocate has focused on breaking these barriers, ensuring that technology serves as a tool for empowerment rather than exclusion. Through my engagement with individuals with disabilities and as the host of Duniyar Fasaha (Fasaha World) on Unity FM, I have worked to bridge the digital divide by providing foundational digital education to marginalized groups. By introducing people with special needs to basic computer skills such as Microsoft Word, Excel, PowerPoint, and internet navigation, I have witnessed firsthand how technology can unlock new opportunities and transform lives. Digital Skills for Special Needs: A Path to Inclusion Inclu...

Yanzu yanzu: 'yan majalisar dattijai sun tafi hutu domin gudanar da yaƙin neman zaɓe

Majalisar dattijan Nigeria, sun tafi hutu a yau Laraba, domin samun cigaba da gudanar da harkokin yaƙin neman zaɓe a jam'iyyun da suke ciki, don tunkarar babban zaɓen shekarar 2023, kamar yadda shugaban majalisar, Sanata Ahmad Lawan, ya bayyana yayin zaman majalisar na wannan rana. Lawan yace zace zasu tafi hutun ne domin tabbatar da abubuwa sun zama cikin tsari a ƙasar nan, kuma za su dawo a ranar 28 ga watan Fabrairu, kwanaki uku kenan bayan an gudanar da zaɓen shugaban ƙasa dana yan majalisun tarayya, kafin su sake tafiya wani hutun a ranar 1 ga watan Maris, domin gudanar da zaɓen gwamnoni da yan majalisun dokokin jiha, da za'ayi a ranar 11 ga watan Maris. Cikin jawabinsa, Lawan yayi kira ga hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC, da kuma jami'an tsaro, akan su tabbatar sunyi ayyukansu yadda ya dace, domin yin zaɓe cikin kwanciyar hankali da lumana, karbabben zaɓe kuma sahihi. Majalisar Nigeriya

All Is Set For APC Presidential Primary.

All is now set for the All Progressives Congress (APC) Presidential primary in Abuja holding from Monday, June 6 to June 7 at the Eagle’s Square with six aspirants in the lead, Jasawa Times learned. The presidentail aspirant include the Vice-President Yemi Osibanjo; former Minister of Science and Technology, Ogbonnaya Onu, Ebonyi Gov. Dave Umahi; former Lagos Gov. Bola Ahmed Tinubu, former Minister of Transportation, Rotimi Amaechi and ex-Minister of State for Education, Chief Chukwuemeka Nwajiuba. The Eagles Square is expected to host about 2,240 delegates from the 36 states and the Federal Capital Territory. Expectedly, the influx of people into the FCT has increased, a development that has attracted more police presence at the Eagles Square and some hotels hosting the delegates and chieftains of the APC. Ahead of the event, the party’s National Chairman, Sen.Abdullahi Adamu on Sunday visited the Eagles Square where he expressed satisfaction with the facilities put in place by...